>

 

... Jarida Mai Ratsa Zukata

Gida  Labarai  Ra'ayi  Shafukan Musamman  Tattaunawa  Dandali  Tsokaci  Kudin Talla   Gamu Da Mu   A Tuntube Mu

A GANINA

 

Litinin 23  zuwa Laraba 25 ga Yuni, 2008

 

 

 

Mutanen Kudan Sun Yi Dacen Shugaba

DIMOKURA[IYYA tsari ne da ke ba jama’a cikakken ’yanci ta hanyar siyasa na su za~i wanda suke bu}ata ko kuma mutum ya sami cikakken ’yancin tsayawa domin jama’a su za~e shi a kan kowane irin matsayi da tsarin mulkin }asa ya bayar da dama ga jama’a, su nema tun daga matakin }aramar hukuma zuwa jiha da }asa baki ]aya wato tarayya.
Sakamakon wannan dama ce ta siyasa a tsarin dimokura]iyya ya sa mutane da dama ke zaune a wurare daban-daban tun daga matakin unguwa zuwa gari da manyan garuruwa da suka zama mazaunin jiha da ake ganin nan ne mazaunin gwamnatin jiha da ke tara al’umma da yawa fiye da sauran sassa.
A wa]ansu wurare, za ka ji irin wa]annan al’umma da suke zaune a wurare daban-daban za ka ji wa]ansu na yin murnar samun ingantaccen shugaban da suka za~a ta hanyar tsarin dimokura]iyya, za ka ji suna murna, wasu kuma suna cikin wani hali na rashin gamsuwa sakamakon rashin samun ribar dimokura]iyya.
Kuma wannan samun riba ko rashin samun ribar dimokura]iyya ya kusa zama ruwan dare a tsakanin al’ummar Nijeriya, saboda za ka ji wa]ansu na kukan cewa, su tun da suka za~i wane a matsayin wakili ko wani da zai ri}e masu wani ofis da ya zama dole sai ta hanyar siyasa ne, za a iya za~en duk wanda zai yi wa al’umma jagora, saboda a wani lokaci za ka ji abin ya zamanto wa]ansu mutane na cigiyar ainihin ]an majalisarsu da suka za~a ta hanyar tsari irin na dimokura]iyya domin ya yi masu ~atan dabo, sun rasa inda za su lalubo shi ballantana kuma su san shirin wane, irin shugabanci ne suke fuskanta.
Ma’ana dai shin yana kare masu bu}atunsu ne ko a’a? Saboda sanin kowa ne irin wannan tsari na dimokura]iyya da ke da ’yancin yi nza~e suka kuma za~i ainihin wanda suke so don yi masu mulki, ko wakilci, su ba su damar su yi idanu hu]u da wakilinsu ko wanda suka za~a sai a matakin }ananan hukumomi a }asar nan baki ]aya.
Saboda wani wakilin in ya tafi Abuja in na tarayya ne, in kuma na jiha ne shi kenan zai tafi ne ya kama yin hidimar gabansa da sunan yana wakiltar wasu jama’a da ya fito daga cikinsu, domin hasalima ma za ka ji a fili yana cewa, shi za~a~~en wakili ne tun da dai ga wata shaidar takarda da ke nuna cewa, an za~e shi daga waje kaza ya zo tarayya ko jiha domin ya wakilce su.
To, a bisa dukkan alamu al’ummar da ke zaune a }aramar hukumar Kudan da ke cikin Jihar Kaduna sun yi dacen shugaba wanda zai yi masu shugabanci daidai da irin bu}atunsu domin share masu hawaye ta hanyar aiwatar masu da aiki kamar yadda ya dace su sami ci gaba. Ka ga kenan a iya cewa al’ummar }aramar hukumar Kudan da ke cikin Jihar Kaduna sun yi dacen shugaba, mai kishin ci gabansu wato Alhaji Abdullahi S. Ahmad.
Shi wannan bawan Allah, Alhaji Abdullahi S. Ahmad mutum, ne da mutanen }aramar hukumar Kudan ba su ta~a samun mutum irinsa ba, domin shi ne ya rungumi jama’a marasa galihu yake tallafa masu ta yadda rayuwarsu za ta inganta, saboda shi ya fito fili ya bayyansu da cewa su ma mutane ne kamar kowa, don haka sun cancanci kowane irin taimako kasancewarsu a cikin wannan }aramar hukuma ta Kudan da ta kasance ]aya daga cikin }ananan hukumomin Jihar Kaduna da ke tarayyar Nijeriya.
Koda irin wannan ka]ai kawai aka tsaya, mutane za su zama shaidar cewa al’ummar wannan }aramar hukuma ta Kudan sun sha bamban da sauran wa]ansu al’ummar da ke ta famar cewa su ba su sami damar da na kan keke zuwa ga masu tafiya a kan babur ko mota kai har ma da masu amfani da jaki da dai sauransu.
Ta ~angaren samar da ilimin makarantar firamare, kai ka ce babu wani wurin da aka ta~a gudanar da wata hidima ta ci gaba sai nan kawai, saboda duk makarantun firamare da ke fa]in }aramar hukumar babu makarantar da ba a kai mata ]aukin ayyukan da suka dace daidai da bu}atarta ba.
Uwa uba kuma sai ta ~angaren }arin albashin malaman makaranta tare da kula da lafiyarsu, duk domin }ara inganta matsayin ilimi a fa]in }aramar hukumar baki ]aya.
A halin da ake ciki, na je na gane wa idanuna irin yadda asibitoci aka wadata su da magunguna iri-iri, kamar dai yadda ya dace a yi ga kowane irin asibitin da ake samun ribar dimokura]iyya a cikinsa kuma manya da yara maza da mata ke ta}ama da shi a duk fa]in Nijeriya baki ]aya.
{aramar hukumar Kudan, }ar}ashin jagorancin Alhaji Abdullahi S. Ahmad ba ta tsaya a nan ba, domin kuwa idan aka dubi irin ]imbin ayyukan raya }asa da aka gudanar domin ci gaban al’umma, nan ma sai a ga cewa, ba a barta ta daga baya.
Daga cikin ]imbin ayyukan da za a iya yi wa makaranta wannan jarida ta Gaskiya Ta Fi Kwabo bayani, sun ha]a da wa]anda aka rigaya aka kammala, yayin da wa]ansu kuma ana nan ana yinsu a halin yanzu, da suka ha]a da hanyar Kudan zuwa [ankado da wadda ta tashi daga Kudan zuwa {auran Wali da Kudan zuwa Garu zuwa La~a ta ~ulla {auran Wali duk domin a sau}a}a wa masu tafiya }asa da masu ababen hawa.
Daga cikin asibitocin da na ziyarta wa]anda ko dai aka gina ko kuma aka yi masu kwaskwarima aka }awata su sun ha]a da na garin Kudan da na [andako da Za~i da Ta~a da na Likoro da kuma wanda yake a garin Hun}uyi. Duk wa]annan asibitoci ana ba su kyakkyawar kulawa don jin da]in al’ummar }aramar hukumar Kudan.
A bisa haka ne na sami damar tattaunawa da wasu jama’a da ke zaune a }aramar hukumar don jin ta bakinsu a game da irin shugabancin shugaban }aramar hukumar, Alhaji Abdullahi S. Ahmad, shin akwai da]i ko a’a?
Sun bayyana mini cewa tun da suka kasance a }aramar hukumar Kudan, ba su ta~a ganin shugaban da ya yi masu aiki irin Ahmad Abdullahi ba. Sun bayyana cewa, dalilin fa]in wannan magana kuwa shi ne, babbar sana’ar da mutanen garin Kudan suke ta}ama da ita shi ne noma. Suka ce a daminar bana an raba takin zamani mai yawa da ba a ta~a raba irinsa a lokacin baya ba, kuma manoma na ha}i}a aka bai wa takin, ba ’yan kasuwa ko ’yan siyasa masu sayar wa a kasuwar bayan fage ba.
Haka abin yake a ~angaren samar da wutar lantarki a }aramar Hukumar Kudan, inda babu wani gari da ke }ar}ashin }aramar hukumar da ba a wadata shi da wutar lantarki ba.
Ko a kwanaki sai da shugaban }aramar hukumar Kudan, Alhaji Abdullahi S. Ahmad, ya gayyaci Gwamnan Jihar Kaduna, Mazayyani Muhammadu Namadi Sambo inda ya je }aramar hukumar Kudan ya }addamar da bayar da bashi ga manoma. Ka ga a nan ma wani ci gaba ne aka samu a }aramar hukumar.
Wa]annan ayyuka da ma wa]ansu da ba a kammala ba, fatarmu dai a nan ita ce Allah Ya }ara ba shugaban }aramar hukumar Kudan, Alhaji Abdullahi S. Ahmad hikima da basira da }wazo da tausayin talakawa na ci gaba da ayyukan alherin da ya soma. Allah kuma Ya kare shi daga ma}iya da mahassada da ’yan hana ruwa gudu.

 

 

©2005 New Nigerian Newspapers Limited.

Webmasters: Emmanuel C. Bello & Suleiman A. Adamu