>
 

 

 

... Jarida Mai Ratsa Zukata

Gida  Labarai  Ra'ayi  Shafukan Musamman  Tattaunawa  Dandali  Tsokaci  Kudin Talla   Gamu Da Mu   A Tuntube Mu

LABARAN CIKIN GIDA

 

Litinin 30 zuwa Laraba 2 ga Yuli, 2008

 

 

Jami’an NDLEA Sun Kamo Tsoho [an Shekara 80

AMINU BALARABE, Daga Gusau

Hukumar hana sha da fataucin miyagun }wayoyi (NDLEA) reshen Jihar Zamfara ta gabatar da wasu da take tuhuma da tu’ammali da miyagun }wayoyi a ofishinta da ke Gusau.
Daga cikin wa]anda ake tuhumar har da wani tsoho mai kimanin shekaru tamani (80) mai suna Garba Maigemu Sabon Garin Gusau wanda ake zargin ya shahara da zama kuncin mashaya.
Garba Maigemu da aka kama yana tare da wani saurayi mai suna Yakubu [an-Mutuwa mai shekara 24.
Ana zargin saurayin yana ha]a baki da tsohon a wajen gudanar da mummunar sana’arsu.
Kwamandan rundunar hana sha da fataucin miyagun }wayoyi a jihar, Alhaji Ibrahim Muhamamd Dodo, ya ce tuni ma’aikatansa suka kama wa]anda ake tuhumar a wani samame da suka kai a wurin da suke gudanar da sana’ar su ta miyagun }wayoyi.
Ya gabatar wa ‘yan jarida da wa]anda ake tuhumar a wani ~angare na bikin ranar ya}i da miyagun }wayoyi ta Majalisar [inkin Duniya wanda aka yi a ofishin hukumar a Gusau, cibiyar Jihar Zamfara.
Alhaji Ibrahim Muhammad Dodo ya ce rundunarsa a shirye take ta ya}i ]abi’un sha da fataucin miyagun }wayoyi a wannan jihar. Ya }ara da cewa, a shekarar da ta gabata sun sami nasarar }wace miyagun }wayoyi da dama daga masu tu’amali dasu.
Ya ce a wannan shekara sun kama ganyen tabar wiwi da nauyinta ya haura kilogirrm ]ari uku da wasu kayan sa maye wadanda nauyinsu ya haura kilogiram ]ari hu]u.
 

 

©2005 New Nigerian Newspapers Limited.

Webmasters: Emmanuel C. Bello & Suleiman A. Adamu