|
|
|
Mataimakiyar Gwamnan Filato Ta {addamar
Da Kwamitin Bun}asa Ilimi
ISA AHMED, Daga Jos
MATAIMAKIYAR gwamnan Jihar Filato kuma kwamishiniyar ilimi ta jihar,
Misis Pauline Tallen, ta }addamar da wani babban kwamiti na mutum 28
da zai bayar da shawarwari a kan hanyoyin da za a bun}asa ilimi a
jihar a gidan gwamnatin jihar da ke Jos, babban birnin jihar.
Da take jawabi a lokacin }addamar da kwamitin, mataimakiyar gwamnan
ta bayyana cewa, duk da ma}udan ku]a]en da gwamnatin jihar ke
kashewa a kan harkokin ilimi a jihar har yanzu akwai }arancin
gine-gine da kayayyakin aiki a makarantun jihar da a sakamakon haka
ilimi ke yin baya a jihar.
Misis Pauline Tallen ta bu}aci kwamitin a kan ya samar da
nagartattun shawarwarin da za su taimaka wajen bun}asa ilimi a jihar.
Ta ce babu shakka gwamnatin jihar ta tashi tsaye wajen ganin ta
bun}asa ilimi a jihar. Kuma ta ]eba wa kwamitin wa’adin shekara ]aya
ya mi}a rahotonsa.
Da yake jawabi a madadin ’yan kwamitin, shugaban kwamitin, Mista
Mataimaki Tom Maiyashi, ya yaba wa gwamnatin Jihar Filato a kan kafa
wannan kwamiti. Ya bayar da tabbacin cewa, kwamitin zai yi iyakar }o}arinsa
wajen ganin ya sauke wannan babban nauyi da aka ]ora masa.
Wannan kwamiti mai mambobi 28 ya }unshi masu ruwa da tsaki a kan
harkokin ilimi na ~angaren gwamnati da masu zaman kansu. Mista
Mataimaki Tom Maiyashi ne yake shugabancinsa a yayin da daraktan
bincike da tsare-tsare na ma’aikatar ilimi ta Jihar Filato, Mista
Laurance Ba}o, ne sakatarensa.
|