>
 

 

 

... Jarida Mai Ratsa Zukata

Gida  Labarai  Ra'ayi  Shafukan Musamman  Tattaunawa  Dandali  Tsokaci  Kudin Talla   Gamu Da Mu   A Tuntube Mu

 

Alhamis 2  zuwa Lahadi 5  ga Oktoba 2008

 

 

Za Mu Ci Gaba Da {o}ari A Kakar Wasanni Ta Bana
–Mai Horar Da Gombe United

MUSA MUHAMMAD KUTAMA, Daga Kalaba
OLADUNMI Oyekale mai horar da }ungiyar wasan }wallon }afa ta Gombe United, ya fa]i a Kalaba cewa }ungiyarsa za ta ci gaba da yin }o}ari a kakar wasa ta bana domin ta bai wa mara]a kunya, kuma ta kia ga cimma buri na lashe duk wasu kofuna a wannan kakar wasa ta bana. Oyekale ya fa]i haka a Kalaba yayin amsa tambayoyin wakilinmu.
Bugu da }ari, domin cimma burin gwamnan Jihar Gombe, Alhaji Muhammadu [anjuma Goje, yana yin iyakacin }o}arinsa a kan }ungiyar don babu abin da za su ce masa sai dai “Allah Ya saka masa da alheri”.
Daga nan sai ya bayyana cewa, fatarsu a wannan shekara su ga sun lashe kofin Premier da na FA.
A wata sabuwa Kodinetan }ungiyar Gombe United, Malam Farouk Yarma, ya bu}aci hukumar tarayyar }wallon }afa ta Nijeriya wato NFF da NFL su sama wa al}alan wasa isasshiyar kariya ta jami’an tsaro da za su ri}a rakosu daga cikin fili zuwa waje a yayin da aka tashi daga wasa.
Malam Yarma ya }ara da cewa, yin haka ne ka]ai zai sanya al}alin wasa ya sami natsuwa, ya gudanar da aikinsa ba tare da wata fargaba ba, musamman ma su al}alan wasan, suna aiki ne da doka da kuma }a’ida ta aikinsu don haka wajibi ne hukumomin biyu su samar masu da ingantacciyar kula ganin cewa, duk iyakacin }o}arin da al}alin wasa ya yi dole wa]anda ba su yi nasara ba a wasa magoya bayansu su ce za su far wa al}alin wasa.
A }arshe, ya yi fatar hukumomin da ke da ruwa da tsaki a harkar za su samar da cikakkun jami’an tsaro saboda kare lafiyar al}alan wasan.

 

 

©2005 New Nigerian Newspapers Limited.

Webmasters: Emmanuel C. Bello & Suleiman A. Adamu