|
An
Tashi Wasan Uni-Rovers Da Bagobiri 1 Da 1
MUSA MUHAMMAD KUTAMA, Daga Kalaba
DUK da kasancewa an tashi kunnen doki a wasan sada zumunta da aka yi
a ranar Lahadi tsakanin }ungiyar wasan }wallon }afa ta UNI-Rovers
wato tsohuwar }ungiyar Kalaba Rovers da takwararta ta Bagobiri FC
wadda ke yin wasa a rukunin ’yan dagaji a filin wasa na U.J. Esuene
da ke garin Kalaba, ya ce nasara ce babba gare su mai horar da ’yan
wasan Bagobiri FC da ke Unguwar Hausawa a Kalaba. Mohammed Idris ne
ya shaida wa wakilinmu haka jim ka]an da kammala wasan sada zumuntar.
Ya ci gaba da cewa wannan canjaras da muka yi da su hakan ya nuna
matakin farko gare mu na shiga gasar cin kofin Gwamnan Kuros Riba
wanda za a fara shi bada da]ewa ba. Da yake wasa samun sa’a ne mai
horar da Bagobiri FC Idris, ya }ara da cewa, “’yan kallo da magoya
bayanmu sun yi tsammanin za a lallasa mu da kamar ci 3 babu ko ]aya
amma sai ga shi an tashi 1 da 1”.
Wakilinmu da ya kalli fafatawar tsakanin }ungiyoyin biyu ya aiko
cewa, a daidai minti na talatin da shida ne UNI Rovers suka samu
dukan daga kai sai mai tsaron gida. [an wasan }ungiyar Bobo Sim ne
ya buga }wallon a dukan fanaritin.
Haka aka ci gaba da yin wasa UNI Rovers na neman }ari, Bagobiri na
neman farkewa, a daidai minti na sittin da takwas, ]an wasan gaba na
Bagobiri FC Wishdom Bassey, ya farke cin da aka yi wa }ungiyarsu
bayan da ya samu sa’ar wuce masu tsaron baya na Uni-Rovers. Haka aka
tashi wasan.
Wakilinmu ya tunatar cewa wannan shi ne wasan sada zumunta na farko
tun kafa }ungiyar Uni-Cem Kalaba wata uku kenan yayin da }ungiyar
Bagobiri FC ta samu ciyarwa gaba daga rukunin da take wasa. An yi
wasan lami lafiya, an tashi kowane na mai cike da farin ciki. |