|
 |
|
|
|
|
Gida
Labarai
Ra'ayi
Shafukan Musamman
Tattaunawa
Dandali
Tsokaci
Kudin Talla
Gamu Da Mu
A Tuntube Mu |
|
MANYAN
LABARAI |
|
Click here to
download Dr. Abdalla Font, A special font for reading Hausa hooked
letters on Computers
 |
|
Litinin 5 zuwa Laraba 7 ga Mayu,
2008: 29 - 1 ga Jimadal-Ula, 1429 B.H |
|
|
|
|
|
DANDALIN
FINA-FINAN HAUSA
Ba Ni Da Wata Ala}a Da Bokaye –Rikadawa
A WANNAN mako, wakiliyarmu SAFIYAH ABDUL{ADIR ta sami
zantawa da shahararren ]an wasan Hausar nan mai suna MUHAMMAD RABI’U RIKADAWA
wanda ake wa la}abi da DILA inda ya zayyana mata yadda ya fara yin harkar fim da
kuma dalilin da ya sa a ganinsa gwamnati ke yi wa masu wannan sana’a ta fim
ri}on sakainar kashi. Ga dai yadda hirar ta kasance:-
GTK: Za mu so sanin da wa muke magana?
RIKADAWA:
Sunana Muhammad Rabi’u Rikadawa ]an wasan Hausa. Ni ]an asalin Jihar Kano ne,
amma an haife ni a garin Kaduna, inda ina da shekaru 5 da haihuwa, mahaifina ya
tura ni wajen wani malami domin yin karatun allo (almajiranci). Bayan na sauke
karatun Al}ur’ani Mai Girma sai na dawo Kaduna na shiga makarantar boko kuma na
yi karatu daidai gwargwado.
GTK: Ko me ya ja ra’ayinka zuwa harkar wasan kwaikwayo?
|
|
|
{ungiyar
‘AWEDI’ Ta Tallafa Wa Al’ummar Musulmi —Sheikh Sulaiman
GTK. A wane lokaci ne kuka kafa wannan cibiya, kuma mene ne manufofin kafa ta?
Sheikh Sulieman To, babu shakka wannan cibiya ta AWEDI, mun fara tunanin kafa ta
ne a farkon watan 1 na shekara ta 2006. Kuma mun ci gaba da tunanin yadda za mu
ha]a tsarinta da abubuwan da za ta tafiyar, domin ya zamo daidai da }a’idojin da
gwamnati ta sanya a kan }ungiyoyi masu zaman kansu.
Mun sami nasarar kar~ar satifiket ]in kafa wannan cibiya a ranar 22 ga watan 11
na shekara ta 2006. Daga wannan lokaci ne wannan cibiya ta kafu kuma ta fara
aiwatar da manufofinta. .
.........ci
gaba
Karantar Da Makiyaya:Kwalliya
Ta Biya Ku]in Sabulu –Hajiya Hajara
GTK: Ko wace ce Hajiya Nana?
NANA:
Sunana Hajiya Nana Hajara Abdul Ahmed. Ni, mutumiyar Maiduguri ce da
ke Jihar Borno. Na yi karatun firamare da sakandare sannan na
kammala karatun digirina a Jami’ar Maiduguri. Kuma ina da aure da
’ya’ya mata biyu, Yusra da Zainab Abdul Ahmed.
GTK: A ina kike aiki kuma me ya sa kike aiki?
NANA: Da farko dai, ina aiki ne da ma’aikatar ci gaban babban birnin
tarayya da ke Abuja wato FCDA. .......ci
gaba |
|
|
|
|
|
|
Waiwaye Kan Rawar Da ’Yar’Aduwa
Ya Taka
Nijeriya
ta yi nisa wajen kafa ginshi}an mulkin dimokura]iyya wa]anda za a ]ora ginin ci
gaban }asa a kansu. Sanin kowa ne cewa babu }asar da za ta yi nasarar ci gaba ba
tare da ta rungumi salon mulkin da ke ba jama’a damar za~en shugabanninsu ba.
Salon mulkin dimokura]iyya shi ke ba jama’a dama su za~i wanda suke so kuma suka
amince masa ya gudanar da al’amurransu na rayuwa.
Haka kuma wannan salo kan ba talakawa dama su taka wa shugabanninsu birki a duk
lokacin da suka lura cewa za su wuce maka]i da rawa. Ta haka ne ake yin maganin
miyagun shugabanni, domin kuwa in ta yi }amari har tsige su ana iya yi daga kan
kujerar mulki.........ci
gaba
|
|
|