|
Gwamna Mahmud Shinkafi Ya Ce:-AHMAD SANI YANA GOYON BAYANA
AN zargi masu baza jita-jita dangane da
rahotonnin da ake yawan samu a kan ~a~ewar dangantaka tsakanin
Gwamna Shinkafi da tsohon Gwamnan Jihar Zamfara, Alhaji Ahmad Sani
Yariman Bakura, a game da manufa da rikicin siyasa.
Gwamnan Jihar Zamfara, Alhaji Mahmud Aliyu Shinkafi, ne ya yi zargin
a lokacin da ya ziyarci kamfanin buga jaridu New Nigerian da Gaskita
Ta Fi Kwabo (NNN) a kwanaki a Kaduna.
Ya fa]i cewa, ba kamar yadda aka ]auka ba, Alhaji Ahmad Sani wanda a
yanzu Sanata ne ya bayyana goyon baya a game da shirye-shiryen da
yake aiwatarwa tun da aka rantsar da shi a watan Mayun 2007.
Shinkafi shi ne mataimakin tsohon gwamna Ahmad Sani na shekara
takwas kuma a kwanakin baya ana bayar da rahotanni kan }azamin
fiti-na-fito a tsakanin magoya bayansu.
Kuma Gwamna Shinkafi ya amince cewa, an ]an sami sa~ani a tsakaninsa
da Sani a baya. Ya ce sun sasanta junansu lami lafiya a sanadiyyar
sanya bakin fitattun dattawa musamman Mai Martaba Sarkin Zazzau,
Alhaji Shehu Idris.
Gwamnan Zamfara ya lura cewa, babu wani da zai iya fa]in takamaiman
abin da ya haddasa rashin fahimta a tsakaninsu don hatta shi ma bai
sani ba. Ya ce, “an dai warware komai”.
“Ba a ta~a samun lokacin da muka yi fito-na-fito ba, abin da ga
alama ake ganin matsala ce shi ne mutane suna yin zantuttukan siyasa
wa]anda ba daidai ba kuma wasu suka ]auke su na tayar da zaune tsaye”,
inji shi.
Gwamna Shinkafi ya ce “ha}i}a, Yarima yana farin ciki da }o}arin da
muke yi a gwamnatina don ciyar da Jihar Zamfara gaba”.
Ya ce wani ~angare ne na sanya bakin manya a kan rikicin shi ne
bu}atar su tsawata wa magoya bayansu a kan su guji ta’annati. Ya ce
da yardar Allah abubuwan da ke kawo masu rarrabuwa sun kau.
Haka kuma ya ce ra]e-ra]in rahotannin cewa, majalisar dokokin Jihar
Zamfara tana shirye-shiryen }addamar da bincike a kan ayyukan
gwamnatin Sani daga 1999 zuwa 2007 ba gaskiya ne ba.
Ya yi bayanin cewa, niyyar ’yan majalisar ita ce gudanar da sanin
dukkan ayyuka da kwangilolin da gwamnatiu da ta gabata ta bayar kuma
ba a kammala su ba.
Gwamna Mahmud Shinkafi ya ci gaba da cewa, akasarin ayyukan na
Gwamnatin Tarayya ne kuma dalilin binciken shi ne don a rubuta
rahoto zuwa ga Gwamnatin Tarayya a kan abin da za a yi don hanzarta
kammala ayyukan.
Ya nuna ba}in ciki a game da ra]e-ra]in. Ya ce “ban san inda mutane
suka sami wa]annan ra’ayoyi ba”.
Gwamna Shinkafi ya ce “babu wasu ayyuka wa]anda ba a kammala su a
zamanin gwamnatin Yarima da na soke su ba. Mutanen da suka fa]i
sa~anin haka, suna ya]a }arairayi ne”.
Ya ce kashi 80 daga cikin ]ari na tsare-tsaren da ya gada daga
Yarima da suka ha]a da ma’aikata da ayyuka suna nan. Ya }aryata wani
rahoto kan ya shirya sallamar ’yan majalisar zartarwa na yanzu
wa]anda daga gwamnatin Sani suke, inda ya ce, “kuna iya tafiya ku
tabbatar ban ta~a wani ba”. |