|
Gwamnatin Sakkwato Ta Ba ’Yan Kasuwa Rancen Naira Biliyan 2
MUSA LEMU, Daga Sakkwato
GWAMNATIN Jihar Sakkwato ta bayar da bashin Naira
biliyan biyu ga ’yan kasuwar jihar domin taimaka masu su ci gaba da
tafiyar da harkokin kasuwancinsu a gida da kuma wajen }asa.
A lokacin da yake }addamar da bikin bayar da rancen ku]in, Gwamnan
Jihar Sakkwato, Alhaji Aliyu Magatakarda Wamakko, ya ce wannan yana
]aya daga cikin al}awurran da ya yi a lokacin }addamar da ya}in
neman za~ensa.
Alhaji Aliyu Magatakarda Wamakko ya ce ana sa ran ‘yan kasuwar su
biya wannan rance cikin watanni 24. Wa]anda suka amfana da rancen
sun ha]a da }ungiyar masu sayar da albasa da sauran kayan ruwa da }ungiyoyi
daban-daban domin samun sukunin bun}asa kayayyakin kasuwanci.
Gwamna Wamakko ya ce gwamnatin jihar ta }ir}iro hanyar bayar da
wannan rance kuma ta umarci Bankin Oceanic da ya bayar da ku]in. Ya
ce gwamnatin jihar za ta biya ku]in ruwa na wannan rance ga Bankin
Oceanic.
Ya kuma tunatar da al’ummar Jihar cewa, tuni gwamnatin jihar ta kafa
wani kwamiti wanda zai duba hanyoyin farfa]o da kamfanoni kamar
kamfanin samar da kayayyakin masarufi da raba wa da kamfanin saka
jari na Jihar Sakkwato da kuma kamfanin ajiya da bayar da rancen
gina gidaje da mallakarsu.
Gwamnan ya yi fatar cewa, jama’ar da suka amfana da wannan rance za
su yi amfani da shi ta hanyar }ara bun}asa tattalin arzi}in jihar
domin rage zaman kashe wando da sauran miyagun ayyuka.
Ya garga]i ’yan kasuwar da suka amfana da wannan rance da su cika
nasu ta hanyar biyan wa]annan basussuka kamar yadda aka tsara
kasancewar gwamnati ta cika nata.
A }arshe, Gwamna Wamakko da mataimakinsa da wakilin mai Alfarma
Sarkin Musulmi da kuma shugaban majalisar dokokin jihar suka raba
zunzurutun ku]i Naira miliyan 36 da dubu ]ari 8, a inda mutane 4
suka sami Naira miliyan 5, wasu Naira miliyan 2, kuma mutane 4 suka
sami Naira miliyan 1 kowannensu, sai kuma hu]u suka sami Naira dubu
200 kowannensu. |