>
 

 

 

... Jarida Mai Ratsa Zukata

Gida  Labarai  Ra'ayi  Shafukan Musamman  Tattaunawa  Dandali  Tsokaci  Kudin Talla   Gamu Da Mu   A Tuntube Mu

MANYAN LABARAI

 

Litinin 30  zuwa Laraba 2 ga Yuli, 2008

 


Gwamnatin Sakkwato Ta Ba ’Yan Kasuwa Rancen Naira Biliyan 2

MUSA LEMU, Daga Sakkwato

GWAMNATIN Jihar Sakkwato ta bayar da bashin Naira biliyan biyu ga ’yan kasuwar jihar domin taimaka masu su ci gaba da tafiyar da harkokin kasuwancinsu a gida da kuma wajen }asa.
A lokacin da yake }addamar da bikin bayar da rancen ku]in, Gwamnan Jihar Sakkwato, Alhaji Aliyu Magatakarda Wamakko, ya ce wannan yana ]aya daga cikin al}awurran da ya yi a lokacin }addamar da ya}in neman za~ensa.
Alhaji Aliyu Magatakarda Wamakko ya ce ana sa ran ‘yan kasuwar su biya wannan rance cikin watanni 24. Wa]anda suka amfana da rancen sun ha]a da }ungiyar masu sayar da albasa da sauran kayan ruwa da }ungiyoyi daban-daban domin samun sukunin bun}asa kayayyakin kasuwanci.
Gwamna Wamakko ya ce gwamnatin jihar ta }ir}iro hanyar bayar da wannan rance kuma ta umarci Bankin Oceanic da ya bayar da ku]in. Ya ce gwamnatin jihar za ta biya ku]in ruwa na wannan rance ga Bankin Oceanic.
Ya kuma tunatar da al’ummar Jihar cewa, tuni gwamnatin jihar ta kafa wani kwamiti wanda zai duba hanyoyin farfa]o da kamfanoni kamar kamfanin samar da kayayyakin masarufi da raba wa da kamfanin saka jari na Jihar Sakkwato da kuma kamfanin ajiya da bayar da rancen gina gidaje da mallakarsu.
Gwamnan ya yi fatar cewa, jama’ar da suka amfana da wannan rance za su yi amfani da shi ta hanyar }ara bun}asa tattalin arzi}in jihar domin rage zaman kashe wando da sauran miyagun ayyuka.
Ya garga]i ’yan kasuwar da suka amfana da wannan rance da su cika nasu ta hanyar biyan wa]annan basussuka kamar yadda aka tsara kasancewar gwamnati ta cika nata.
A }arshe, Gwamna Wamakko da mataimakinsa da wakilin mai Alfarma Sarkin Musulmi da kuma shugaban majalisar dokokin jihar suka raba zunzurutun ku]i Naira miliyan 36 da dubu ]ari 8, a inda mutane 4 suka sami Naira miliyan 5, wasu Naira miliyan 2, kuma mutane 4 suka sami Naira miliyan 1 kowannensu, sai kuma hu]u suka sami Naira dubu 200 kowannensu.

 

 


©2005 New Nigerian Newspapers Limited.

Webmasters: Emmanuel C. Bello & Suleiman A. Adamu