>
 

 

 

... Jarida Mai Ratsa Zukata

Gida  Labarai  Ra'ayi  Shafukan Musamman  Tattaunawa  Dandali  Tsokaci  Kudin Talla   Gamu Da Mu   A Tuntube Mu

MANYAN LABARAI

 

Litinin 16 zuwa Laraba  18 ga Nuwamba, 2009

 

PDP Za Ta Yi Shekara 60 A Bisa Mulki — Ogbulafor
— Gwamna Namadi Ya Tallafa Wa ’Ya’yanta

MOHAMMED ADAMU, Daga Kaduna
A LOKACIN da Gwamna Namadi Sambo ya rabar da kayayyakin rage ra]a]in talauci a ci gaba da shirinsa na kyautata wa al’umma, shugaban jam’iyyar PDP na }asa, Cif Vincent Ogbulafor ya da]a jaddada aniyarsu na ci gaba da mulkin }asar nan har na tsawon shekaru 60.
Shugaban ya yi wannan batu ne a dandalin Murtala Muhammad da ke Kaduna a yayin wani taro da gwamnatin Jihar Kaduna }ar}ashin jagorancin Gwamna Namadi Sambo ta shirya don rabar da kayayyakin rage ra]a]in talauci.
Cif Vincent ya ce, gwamnatin PDP a tarayya da jihohi na aiwatar da ayyukan da za su ciyar da }asar nan gaba. Shugaban ya ce, nan da }arshen wannan shekara, gwamnatin Umaru Musa ’Yar’Aduwa za ta samar da wutar lantarki mai megawatt dubu shida.
Don haka sai shugaban ya shawarci masu }alubalantar jam’iyyar da cewar, babu wata riba a irin wannan hali. Shugaban wanda ya kar~i wa]anda suka canza she}a daga wasu jam’iyyu zuwa PDP, ya shawarci mutanen da kada su nuna wani damuwa a zuciyarsu, saboda babu bambanci tsakaninsu da ‘yan jam’iyyar wa]anda suka canza she}a da ma can ‘yan jam’iyyar PDP ne, suka koma AC sun ha]a da Injiniya Bawa Magaji da Dokta Bala Usman da kuma sauran da suka fito daga jam’iyyar ANPP da PDP da kuma PRP.
Tun farko a jawabinsa, Gwamnan Jihar Kaduna ya ce, duk ]an jam’iyyar PDP daga ko’ina idan ya zo Kaduna, ya zo gida ne, saboda haka inji gwamnan a daidai lokacin da suke ba da kayan yanke talauci, suna kuma marhaba da tsofaffin ‘yan jam’iyyar PDP.
Gwamna Namadi ya fa]i cewar, gwamnatinsa na taka rawar gani ta fannoni da dama da suka ha]a da ~angarorin ilimi da gona da kiwon lafiya da tsaro da samar da abubuwan more rayuwa.
Abubuwan da aka raba sun ha]a da motoci da babura da tarakita da gidajen sauro da kayayyakin asibiti da kekunan ]inki. Sauran sun ha]a da kekunan sa}a da fanfon ban ruwa da injunan ni}a da hulunan ]wano.
Sauran manyan ba}i da suka yi jawabi sun ha]a da shugaban jam’iyyar PDP na shiyyar arewa maso yamma da kakakin majalisar dokokin Kaduna, Honorabul Ahmed Hassan Jumare da Alhaji Tijjani Ramalan da Suleiman Hun}uyi da Sanata Isaiah Balat da Sanata Musa Bello.
 

 

 

 


©2005 New Nigerian Newspapers Limited.

Webmasters: Emmanuel C. Bello & Suleiman A. Adamu