>

 

 

... Jarida Mai Ratsa Zukata

Gida  Labarai  Ra'ayi  Shafukan Musamman  Tattaunawa  Dandali  Tsokaci  Kudin Talla   Gamu Da Mu   A Tuntube Mu

MANYAN LABARAI

 

Alhamis 17 zuwa Lahadi 20 ga Yuli 2008

 

Sanata Waku Ya Yi Allah-Wadai Da Jingine Soke Za~en David Mark

ISAH AHMED DAGA JOS
Wani tsohon Sanata daga Jihar Binuwai Sanata Joseph Waku, ya yi Allah- wadai da hukumcin da kotun ]aukaka kara da ke Jos ta yanke na jingine hukumcin soke za~en Sanata mai wakiltar maza~ar Binuwai ta Kudu kuma shugaban Majalisar Dattijai, Sanata David Mark da kotun sauraron }ararrakin za~e da ta yi zama a garin Makur]i ta riga ta yi na soke za~en kujerar Sanatan a ranar Talatar nan da ta gabata.
Sanata Joseph Waku ya yi Allah- wadai da wannan hukuncin ne bayan da kotun ]aukaka }arar ta yanke hukuncin a lokacin da yake zantawa da ’yan jarida a harabar kotun.
Sanata Waku wanda shi ne jagoran masu mara wa Alhaji Usman [an Abubakar Mai Shanu na Jam’iyyar ANPP baya a kan wannan Shari’a ya yi bayanin cewa, wannan hukumci da kotun ta yanke na jingine hukuncin da kotun sauraron }ararrakin za~e ta riga ta yi, kisan gilla ne ga Shari’a a }asar nan. Ya ce hukuncin da kotun sauraron }ararrakin za~en ta yanke na soke wannan za~e ta yi shi ne a kan hujja.
Tun da farko dai kotun ]aukaka }arar da ke Jos ta jingine hukuncin da kotun sauraron }ararrakin za~en ta yanke na soke wannan za~e a zaman da ta yi a ranar Talatar.
Da take karanta yanke wannan hukunci wadda ta yi sama da awa 2 tana karantawa, Mai Shari’a Zainab Bulkachuwa ta ce hukuncin da kotun sauraron }ararrakin za~en ta yanke a kan wannan za~e na Shugaban Majalisar Dattijai Sanata David Mark ta yi shi a bisa kuskure. Ta ce tun da farko kotun sauraron }ararrakin za~en ta yi kuskure da ta }i amicewa da hujjar da Lauyan Sanata David Mark ya gabatar mata na sakamakon za~en }ananan hukumomi 2 a cikin }ananan hukumomi guda 9 da ake da su a wannan maza~a, ta yi gaban kanta ta yanke wannan hukunci.
Mai shari’a Zainab Bulkachuwa ta yi bayanin cewa, tun da an riga an rubuta sakamakon za~en wa]annan }ananan hukumomi a cikin takardun hukumar za~e ta INEC, a doka ba daidai ba ne Jami’in za~en ya soke sakamakon wannan za~e ba.
Ta ce tun da an riga an rubuta sakamakon wannan za~e a tashoshin da aka gudanar da wannan za~e kuma dukkan wakilan Jam’iyyu sun sanya hannu, to, jami’in za~en ba shi da ikon soke sakamakon wannan za~e.
Don haka sai mai shari’a Zainab Bulkachuwa ta ce wannan ]aukaka }ara da Sanata David Mark ya yi yana da hujja. A kan haka ta ce kotun ]aukaka }arar ta jingine wancan hukunci da kotun sauraron }ararrakin za~en ta yanke a ranar 28 ga watan Fabrairun da ya gabata na soke wannan za~e na Sanata David Mark.
Yanke wannan hukunci ke da wuya sai magoya bayan Sanata David Mark suka fara sowa da rungume juna da ka]e-ka]e da raye da raye a harabar wannan kotu.
Da yake zantawa da ’yan jarida bayan yanke wannan hukunci, Lauyan Sanata David Mark cewa ya yi “muna matu}ar farin ciki da wannan hukunci”. Ya ce “a ganina wannan hukunci ya }ara mutunci da }imar sashin shari’a a Nijeriya”.
Shi ma da yake zantawa da ’yan jarida, Lauyan Alhaji Usman [an Abubakar Mai Shanu Robert Clark ya ce a duk inda ~angarori biyu suke ya}i dole ne ~angare ]aya ya sami nasara. Ya ce “mu dai mun yi iyakar }o}arinmu amma a kwana da sanin cewa ko ba da]e ko ba jima gaskiya za ta yi halinta a kan wannan kujera”.
A zaman wannan kotu dai shugaban Majalisar Dattijan Sanata David Mark da Alhaji Usman [an Abubakar Mai Shanu dukkansu ba su sami halartar zaman kotun ba. Amma wata tawaga a }ar}ashin jagorancin tsohon gwamnan Jihar Jigawa, Sanata Saminu Turaki da ta }unshi Nicholas Ugbane da Emmanuel Okpede da Kanar Baba Nyam da Alhaji Sule Audu da Ambasada Ogbe Ogbande da Abba Omoru da kuma Agbo Oghah ta wakilci Shugaban Majalisar Dattijan.



 

 

©2005 New Nigerian Newspapers Limited.

Webmasters: Emmanuel C. Bello & Suleiman A. Adamu