>
 

 

 

... Jarida Mai Ratsa Zukata

Gida  Labarai  Ra'ayi  Shafukan Musamman  Tattaunawa  Dandali  Tsokaci  Kudin Talla   Gamu Da Mu   A Tuntube Mu

RAHOTON MUSAMMAN

 

Litinin 30 zuwa Laraba 2 ga Yuli, 2008

 

Yadda Ake Banka]o Bayanan Albuzzaranci Da Facaka Da
Dukiyar Al’ummar A Kwangilolin Jihar Zamfara

A farko farkon hawansa bisa ga karagar mulkin gwamnatin Jihar Zamfara, Gwamna Ahmed Sani (Yariman Bakura), ya tabbatar wa Zamfarawa cewar shigowarsa cikin mulki na da manufar ganin an inganta rayuwar al’ummar Jihar Zamfara tare da tabbatar musu da samuwar ababen more rayuwa da inganta ayyukan yau da kullum.
Shekaru tara bayan saukarsa daga karagar mulkin jihar, sai ga shi kuma yanzu majalisar dokokin jihar ta fara banka]o wasu bayanai, wa]anda ke nuna gwamnatin Yarima ta yi facaka da dukiyar al’umma ga kuma rashin bin }a’aida wajen bayar da kwangiloli, inda aka bayar da wasu kwangiloli ba takardun yarjejeniya, abin da ya sa~a wa }a’iadar aiki da doka ko kuma ‘Due Process’, a Turance.
Duk hakan ta faru sakamakon zargin sharholiya da dukiyar talakawa da wasu manyan jami’an gwamnatin Yarima da yanzu haka ke cikin wannan gwamnatin ta Mahmuda Aliyu Shinkafi suka yi. Wannan abin da suka yi ta amfani da wannan damar wajen facaka da kuma wawurar dukiyar talakawa abin kunya da takaici ne.
Tun farko dai a baya Babban Bankin Nijeriya ya ta~a fitar da wani bayani a cikin shekarar 2004 zuwa 2005, inda ya ce, Jihar Zamfara ta kasance jiha ta biyu a sahun jihohin da suka fi yawaitar talauci a Nijeriya, kuma jiha ta hu]u da ke da ha]arin gudanar da kasuwanci da sanya hannun jari sakamakon cin rashawa da kuma cewar ba tsayayyen mataki na bin }a’aida ga fitarwa da shigar da ku]a]e a cikin baitulmalin gwamnati.
A }ididdigar da hukumar kula da }ididdigar ci gaban kasuwanci ta Nijeriya ta yi a shekaru uku na tsakanin shekarar 2004 zuwa 2007 ta tabbatar da Jihohin Zamfara da Jigawa da Yobe da Kebbi da Ebonyi da Oyo da  Gombe da Bayelsa da kuma Anambara a matsayin jihohin farko da suke da hatsari ga ci gaban inganta rayuwar al’umma da kulawa da ci gaban kasuwanci da sanya jari ga al’ummarsu.
Wa]annan bayanan duk na masana ne wa]anda ke ganin wa]ansu ababe ba su tafiya daidai a  wasu wurare kuma sun fitar da bayanansu ba domin }iyayya ko }auna ba, sai domin tabbatar da gaskiyar ababen da ke faruwa domin a yi gyara.
Wannan ne ya kawo mu ga  batun binciken da majalisar dokokin Jihar Zamfara ta }addamar a kan ayyukan da gwamnatin Jihar Zamfara }ar}ashin jagorancin Gwamna Ahmed Sani Yarima. Wannan bincike an fara shi tun kusan watanni biyar da suka gabata, lamarin ya yi zafi ne sakamakon ganin yadda wasu bayanan ke }ara tabbatar  da cewar ba a aiwatar da wasu ayyukan a-zo-a-gani na ku]a]en da aka ce an kashe ba, musamman idan an kamanta da irin ma}udan Biliyoyin Nairori da aka ~atar.
Musamman wuraren da majalisar ta fi mayar da hankali a kan bincikenta sun }unshi ayyukan hanyoyi da lafiya da ilmi da ruwan sha da kuma wutar lantarki. Akwai kuma takin zamani da motocin tarakto da aka sayo da kuma sauran ababen da aka kashe ma}udan ku]a]en gwamnati wajen aiwatarwa amma ana zargin babu su a fili.
A bayanan da suka fara fitowa ana zargin gwamnatin Ahmed Sani Yarima da facaka da ku]a]en jama’a wajen biya da shirya gangamin taron siyasa da kuma na kamfen na shugaban }asa, wanda shi tsohon gwamnan ya nemi tsayawa tun da farko.
An bayyana cewar gwamnatin Ahmed Sani Yarima ta ~atar da zunzurutun ku]i har kusan Naira Biliyan biyu da ]ari shidda ga ayyukan tallar takarar shugabancin }asa na ANPP da kuma bayar da ku]a]en kyauta, sai kuma yin wasu ayyuka da ba su shafi al’ummar Jihar Zamfara ba, wa]anda aka rarraba tare da biyan ku]a]e ga wasu jama’a domin sanya zanen hoton Gwamna Ahmed Sani Yarima na takarar shugabancin }asa ga gidajensu a kusan ko’ina a Nijeriya.
Kodayake wasu na ganin yana da wuya a yarda da wannan zargin, wannan abin na da tayar da hankali, idan an kimanta halin da mafi rinjayen matasan Jihar Zamfara wa]anda ke neman tallafi suke ciki ko kuma yadda suke bu}atar ku]a]en da za a tallafa musu ga karatunsu a makarantun gaba da sakandare da wa]anda ke a sakanadare.
Jihar Zamfara dai tana da }ananan hukumomin mulki guda goma sha hu]u, daga cikin yawan wa]annan }ananan hukumomin mulkin guda uku ne kawai ke kusa da babban birnin jihar, wato Gusau.
{ananan hukumomin mulkin kuwa su ne Gusau da Tsafe da Bungu]u. Daga cikin wa]annan }ananan hukumomin mulkin ba ko ]aya wadda aka ha]a ta da layin ruwan sha na famfo daga gidan ruwa na Gusau, a baki ]ayan shekaru takwas da Yariman Bakura ya yi yana mulki, inji wata majiyar majalisar.
Ha}i}a, wannan bincike wanda kwamitin musamman da majalisar dokokin Jihar Zamfara ta kafa na banka]o bayanan da za su taimaka ga fitar da gaskiyar yadda tsohuwar gwamnatin Yarima ta yi amfani da dukiyar jama’a a tsawon lokacin wa’adinta bisa karagar mulki.
Irin }orafe-}orafen da wasu ke fa]a cewar wai ga alama ana wannan binciken ne domin tozarta tsohon gwamna Ahmed Sani da kuma wasu mu}arrabansa, ba komi ne ba, illa borin tukunya. Domin kuwa kamar yadda Shugaban babban kwamitin binciken na majalisar dokokin, Alhaji Murtala Adamu Jangebe, ya bayyana, ba ruwan wannan binciken da wata maganar tozarta wani, illa dai ‘yan Majalisa suna gudanar da aikin da tsarin mulki ya ba su da ma kuma ya tanada musu, ba wata magana illa iyaka.
Binciken ya fara gano cewar mu’amalar da aka yi da ku]a]en talakawa a lokacin tsohuwar gwamnati ya kauce }a’ida, kuma yanzu ne lokacin da za a yi gyaran wannan }a’idar, domin tabbatar da ita ga al’umma. Muddin ana son ci gaba ga al’ummar Jihar Zamfara, dole ne a yi gyaran matsalolin da aka riska na albuzzaranci da facaka da dukiyar talakawa ba bisa }a’ida ba. Ha}i}a, wannan ya yi daidai domin kuwa zai gyara tafiyarta gaba.
Shi kansa shugaban masu rinjaye na majalisar dokoki jihar, Malam Mani Malam Mummuni Masamar Mudi, yana ganin dacewar wannan binciken, domin kuwa zai taimaka wa wannan gwamnati ta yanzu, wajen tabbatar da adalci da kuma gaskiya ga lamurran mulkinta. Hakan in ji, Mani Malam Mummuni shi ne muhimmin gyara ga ci gaban jiharmu ta hanyar bayyana gaskiyar yadda lamurra suka gudana a baya domin amfanin gaba.
Muhimman ayyukan da za a fi kulawa ga binciken, inji wata majiya ta cikin majalisar, sun }unshi kwangilolin hanyoyi da asibitoci da ruwan sha da lantarki da samar da kujeri da kuma tebura ga makarantun firamare da na sakanadare. Kayan noma da  sauran ababen da aka bai wa muhimmanci ga ci gaban al’umma.
Baya ga ‘yan majalisa akwai su kansu manyan jami’an gwamnatin Jihar Zamfara wa]anda suke ganin dacewar wannan aiki, wasu da yawa daga cikinsu a lokacin gabatar da shaida gaban kwamitocin binciken guda biyu, sun jinjina wa ‘yan majalisa kan soma wannan bincike tun tafiyar wannan sabuwar gwamnati ba ta yi  nisa ba, domin tabbatar da adalci  ga al’ummar Jihar Zamfara baki ]aya.
Kamar yadda bayanin da mataimakin shugaban majalisar dokokin jihar, Murtala Adamu Jangebe ya yi, ya tabbatar cewar “Wannan binciken zai kwashe kusan watanni uku ko ma fiye, kuma zai fi mayar da hankali ne ga irin yadda tsohuwar gwamnatin Ahmed Sani Yariman Bakura ta aiwatar da mulkinta ga hanyoyin da suka shafi rayuwar al’umma.
Ya nuna cewar wannan bincike, zai ta~o matsalar ku]a]en da aka kashe wajen bayar da kwangila da kuma yadda aka bayar da wa]annan kwangilolin da wa]anda aka bai wa kwangilar da kuma irin yanayin aikin da suka yi a wa]annan kwangilolin.
Haka ma za a binciko bayanan takardun yarjejeniya na ayyukan kwangilolin wa]anda aka bayar da kuma inda kwangilolin suke. Sai kuma tabbatar da matsayin yanayin aikin da aka yi da kuma darajarsa da wuraren da aka fa]i an yi wa]annan ayyukan.
Akwai kuma zancen hanyoyin da aka bi na aiwatar da ayyukan na gaskiya da wa]anda ma babu, domin tantance lamarin bai ]aya ga al’ummar jihar. Wannan kuwa zai ]auki lokaci ga su, ‘yan majalisar wa]anda za su ziyarci ayyukan domin gani da idonsu, tare da tabbatar da nagartar aikin da aka yi.
Wannan binciken da aka yi wa la}abin ‘Gani Ya Kori Ji’, zai samar da ingantaccen tafarki na bai wa al’ummar Jihar Zamfara dama ga sanin ababen da suka faru a lokaci da kuma }arshen tsohuwar gwamnatin Jihar Zamfara ta Gwamna Ahmed Sani, domin gano gaskiyar al}ibalar ayyukan na raya }asa da ci gaban al’umma da ake nuna samuwarsu.
Ba shakka a }arshen zaman wannan kwamitin, al’ummar Jihar Zamfara za su fahimci gaskiyar inda tun farko gwamnatin Ahmed Sani Yarima ta fuskanta, sakamakon yadda tun farko ake zargin cewar an kasa gudanar da ayyukan raya }asa da kuma samar da ci gaban al’umma a maimakon irin yadda gwamnatin ta ke fuskantar zargin albuzzaranci da yin sama-da-fa]i da dukiyar talakawa a tsawon shekaru takwas na mulkin Jihar Zamfara.
Wani abin sha’awa ga wannan binciken shi ne kusan duk mafi rinjayen ‘yan majalisar dokokin Jihar Zamfara sun nuna amincewarsu a kan binciken, tare da kuma da nuna goyon bayan gayyatar masu ruwa da tsakin gwamnati, wa]anda suka kula da gudanar da tsohuwar gwamnatin Ahmed Sani yanzu kuma suna cikin wa]anda ke damawa a ta yanzu.
Kamar yadda shugaban masu rinjayen majalisar, Alhaji Mani Mallam Mummuni, ya }ara tabbatarwa, “babu wani da za a rufe dangane da wannan binciken, za a binciko lamurran da suka shafi jama’a, kuma za a bai wa jama’a su yi al}alanci tare da hukunta masu laifi a gaban hukumar da aka kafa.
Alhaji Mani Malam Mummuni ya bayar da tabbacin cewar, ba shakka wannan binciken na gaskiya ne, kuma ba wani ja da baya sai har an kamalla shi. [an majalisar wanda ke wakiltar maza~ar Bukkuyum, ya ci gaba da cewar “A yau kam, ba wani da zai zo Jihar Zamfara ya yaudari jama’a, ya tafi da dukiyar su, mu, ‘yan majalisa shi mu }yale shi ko wane ne.
 Ba wani tunanin tsoro ko jin kunya a kan }wato ha}}in al’ummar Jihar Zamfara (inji Mani Malam Mummuni) lamarin wannan bincike abu ne da ya shafi kowa, ba wata saniyar ware, dole ne ‘yan kwangila da jami’an gwamnati su amsa tambayoyin da suka shafi ayyukansu.
Duk dai yadda wannan lamarin ya kasance ba shakka, wannan binciken zai banka]o bayanan sirri wa]anda aka hana jama’ar Jihar Zamfara su gani.
Sai dai kuma abin tambaya a nan shi ne shin yaya makomar wa]anda aka samu da laifi a cikin wannan albuzzaranci da kuma facaka da dukiyar al’ummar Jihar Zamfara za ta kasance, musamman ma ‘yan kwangilar da ake zargin suka lashe dukiyar kwangilolinsu amma ba komi a }asa da kuma jami’an gwamnatin da yanzu ke damawa a cikin wannan gwamnatin?
Shin ‘yan majalisar za su iya rufe ido kuwa, su hukunta kowa har ma da wa]anda yanzu tsulliyarsu ta ]uri ruwa, suka fara kamun }afa ko suke bayyana wa duniya cewar su ba su da masaniyar abin da ake ciki a tsohuwar gwamnati?
Wannan amsar ce, mataimakin shugaban majalisar dokokin, Alhaji Murtala Adamu Jangebe, ya amsa da cewar, “Ba wani wanda ya fi }arfin doka, duk wanda muka gano ya kar~i aiki, ya kuma yi wasa da shi bai aiwatar ba, hukuma za ta hannunta shi bayan kamalla bincike, kuma mu gabatar wa gwamnati da bu}atunmu domin hukunta shi”
Alhaji Murtala ya }ara tabbatar da cewar za a yi adalci wajen binciken, domin haka masu ya]a jita-jita a kan wata barazana su ji tsoron Allah su bari, domin wannan ba zai tayar da hankalinsu ga aikin da aka ba su ba.
Ba shakka dai babbar fatar da ake yi wa wannan kwamitin shi ne ya tabbatar da gaskiya da adalci a tsakanin wa]anda yake bincike, domin zama abin tarihi da kuma samar da ci gaba ga Jihar Zamfara.
Dole ne wannan kwamitin ya raba aya da tsakuwa cikin fahimta da hankali, kada a yi saurin yin da-na-sani wajen hukunta wasu ko hana hukunta wasu domin ra’ayin siyasa ko kuma neman suna. Wannan ne zai iya tabbatar da adalcin majalisa a shekaru hu]u da za su kasance nan gaba.
A yi hattara!!

Dingyadi, Lamba 88 Titin Emir Yahaya, Sakkwato.
 

 

©2005 New Nigerian Newspapers Limited.

Webmasters: Emmanuel C. Bello & Suleiman A. Adamu