>
 

 

 

... Jarida Mai Ratsa Zukata

Gida  Labarai  Ra'ayi  Shafukan Musamman  Tattaunawa  Dandali  Tsokaci  Kudin Talla   Gamu Da Mu   A Tuntube Mu

TSOKACI

 

Alhamis 31  zuwa Lahadi 3 ga Agusta 2008

 

 

   

Rikicin Siyasar Zamfara: Ko Yarima Da Shinkafi Za Su Koyi Darasi?

A yanzu kam ta fito fili na wutar }iyyaya da rikici wadda ke ci gaba da ruruwa a tsakanin tsohon Gwamnan Zamfara, Alhaji Ahmed Sani Yariman Bakura da kuma Gwamna Mahmuda Aliyu Shinkafi. Wannan rikicin siyasa ya ]auko sabon salon kan yadda ake amfani da bangar siyasa domin neman huce fushi da cimma manufa ta yi wa zaman lafiyar Jihar Zamfara barazana.
Rashin ga-maciji da ke tsakanin shugabannin biyu ya fara kai ma}ura ne sakamakon irin yadda magoya bayansu ke jifar juna da manganganun ~atanci na Allah wadai da kuma suka a kan manufofin shugabannin, abin da ake kamantawa da cewa, ya fara zafi.
Rashin jituwa tsakanin Sanata Yarima da tsohon mataimakinsa, Gwamna Shinkafi, ya samo asali ne jim ka]an bayan shigowar sabuwar gwamnati ne, inda ake zargin }o}arin katsalanda wajen gudanarwa da tsohon Gwamna Yarima yake yi wa gwamnatin Shinkafi.
Kodayake lamarin ya fara ne kamar wasa, sai ga shi ‘}aramar magana ta koma babba’, tun tafiya ba ta yi nisa ba, an fara raba hannun riga tsakanin juna. Duk da yake a lokaci mai tsawo, shugabannin sun fito sun }aryata wata rashin jituwa tsakaninsu.
Tsohon Gwamna Ahmed Sani ne ya fara }aryata jita-jitar a lokacin da ya ziyarci ofishin jaridar Trust da ke Abuja. Ya fito fili ya tabbatar wa duniya cewa, Gwamna Shinkafi }anensa wanda ya rena kuma har yanzu yake goya masa baya ga duk manufofinsa. Domin haka, inji Yarima, “ba wani sa~ani tsakaninmu, illa dai surutan mutane ne da ke son janyo matsala ga juna”.
Shi kansa Gwamna Mahmuda Shinkafi ya fa]i irin wannan a hirarsa da jaridar Gaskiya Ta Fi Kwabo a Kaduna, cewa da shi da Yarima uwa ]aya uba ]aya ne, kuma ainihi Yarima na goyon bayan gwamnatinsa, domin haka ba wani sa~ani ko rashin fahimta tsakaninsu.
Haka ma baki da baki Gwamna Shinkafi ya shaida mini a wata hirar da muka yi a cikarsa shekara ]aya bisa karagar mulkin Jihar Zamfara cewa, yana mamaki na masu kawo surutan ba su ga maciji da shi da tsohon mai gidansa, Yarima, domin tun farko shi ba mutum ne mai surutu ko ]aukar tsegumi ba. A ra’ayinsa wannan jita-jitar ana ya]a ta ne domin cimma wata manufa ta samun abinci da haddasa ru]u da fitina tsakanin shugabanni.
Gwamna Shinkafi ya ce, “ba wani dalilin da zai sanya in cuci Yarima domin tun farko na bi Yarima kuma na yi masa ]a’a. Allah Ya hana cuta, Ya kuma hana ka bari a cuci wani. To, yaya zan fa]i wani mugun kalami a kan Yarima”.
Gwamna Shinkafi ya rufe da cewa, “idan har ka tambayi Yarima, abin da na yi masa, ba zai ce ga shi ba, haka ni ma idan ka tambaye ni, mene ne tsakanina da shi, ba zan fa]a ba”.
To, sai dai abin mamaki wannan duk ta canza domin kuwa kowanensu ya fito fili yanzu ya nuna cewa, ba shiri a tsakaninsu, kuma duk wani abin da ake ~oyewa na rashin fahimtar ya bayyana.
Tsohon Gwamna Ahmed Sani Yariman Bakura dai yana zargin Gwamna Shinkafi da mu}arrabansa da kauce wa al}awarin da suka yi na samar da fahimtar juna da ha]in gwiwa wajen aiwatar da gwamnati a tsakaninsu.
Haka ma ya yi zargin cewa, ana }untata wa magoya bayansa ta hanyar kora daga aiki da kuma tsare wasu a gidan yari ba tare da wani dalili ba duk a sakamakon adawarsu ga wasu manufofin Gwamnatin Mahmuda Shinkafi.
Haka ma Yariman Bakura na ganin ba a yi masa adalci ba na yadda aka raba wasu mu}amai na siyasa a }ananan hukumomin mulki da kuma shugabancinsu ba tare da tuntu~ar sa ko ba shi dama ba.
Ahmed Sani Yarima Bakura ya shafe shekaru takwas yana mulkin Jihar Zamfara, kuma a tsawon lokacin mulkinsa ya fuskanci rikita-rikitar siyasa iri-iri ta rashin ingantacciyar manufa wajen aiwatar da tsarin ci gaban al’umma da kuma zargin watsi da bin }a’ida a cikin mulki.
A tsawon mulkinsa, ana zargin ya fi mayar da hankali ne ga cika aljifan magoya bayansa da sauran ‘yan maular siyasa, maimakon aiwatar da ayyukan raya }asa da kuma ci gaba a Jihar Zamfara. Wannan kuwa ya janyo talauci mai yawa a cikin ‘yan siyasa da al’umma.
Wa]anda suke da masaniya kan Yariman Bakura sun tabbatar da cewa, ba ba}on rikicin siyasa ne ba, sai dai yana da saurin hannu wajen shawo kan matsala fiye da duk wanda ke cikin gwamnatinsa. Haka ma Yariman Bakura na da kusanci da kafofin ya]a labarai saboda yadda ya yi tashe kan batun }ir}iro shari’a lokacin mulkinsa.
Yarima ya fuskanci adawa ta zahiri a ciki da wajen gwamnatinsa daga wasu da ke ganin bai dace na yadda yake mulkin jihar ba, duk da yake daga cikinsu ne suka yi sanadiyyar hawansa bisa karagar mulki. Daga cikinsu akwai marigayi Abubakar [akingari, Ibrahim Nabature Nahuce, Sanata Sa’idu Dansadau, Aliyu E.S Mafara, Isan Mayana Gusau, Ibrahim Ruwan Dorawa, Mu’azu Mayana, Salihu Maibuhu Gummi, Sanata Lawal Shu’aib da sauran wasu da suka riga mu gidan gaskiya ko kuma ke da rai har yanzu.
Abin tambaya a nan shi ne shin Yarima ya zama gangar rikici ne wadda ba ta iya zama sai an buga. Babbar matsala ]aya ita ce gano ainihin tushen haddasa matsalar da kuma abin da ya janyo wannan gaba da juna.
Wasu masu nazarin siyasar Zamfara na ta’alla}a wannan kan faruwar ababe da yawa, masu muhimmanci, su ne zargin katsalanda da kuma yawan gori da tsohon gwamna Yarima ke yi wa Shinkafi a cikin gwamnatinsa. Wasu kuma na ganin irin ayyukan ci gaba da raya }asa wa]anda ya dace tun farko Yarima ya aiwatar, amma yanzu kuma Gwamna Shinkafi yake gudanarwa. Wannan na ba}anta rayukan magoya bayan Yarima.
Na }arshe wanda shi ne, tamkar gaskiyar lamari, shi ne tseguma da kuma munafucin siyasa da ya]a jita-jitar da ake yi, ne tushen wannan matsala ganin yadda wasu daga cikin magoya bayan shugabannin biyu ke ya]a jita-jita ko kuma ke }ir}iro da }arerayi a kan juna.
Wannan matsala da dalilan ne suka haddasa dakatar da wasu manyan jami’an gwamnati a baya, ya sanya ~angaren Yarima ganin cewa, Gwamna Mahmuda Shinkafi ya sa~a al}awarin raba daidai na aiwatarwa ta gwamnati, da kuma janyo ruruta wutar fitina da haddasa mummunan rikici a kan juna.
Wasu daga cikin dalilan kuwa sun }unshi binciken gano yadda aka kashe ma}udan ku]a]e ba tare da wani abin a-zo-a-gani ba a kan wasu kwangiloli a lokacin gwamnatin Yarima wanda Majalisar Dokokin Jihar Zamfara ke yi, sai kuma sake bayar da wasu kwangiloli da sake fasalta su da gwamnatin Mahmuda Shinkafi ta yi.
Akwai canjin wuraren aiki masu tsoka zuwa wasu wurare da ake yi wa la}abi na ya-ku-bayi, ko kuma kulawa ta ‘ya’yan Mowa da na Bora da ake zargin ana yi wa wasu jami’an gwamnati da ke da biyayya ga Yarima, duk sun }ara taimakawa kan ya]a labarai na cewa, Gwamna Shinkafi na }o}arin tozarta Yarima da magoya bayansa. A dalilan wannan, an }ara zurfafa wannan fitina.
Farkon wannan rikici tsakanin Yarima da Shinkafi, wasu muhimman mutane a cikin }asa sun yi }o}arin sassantawa domin kauce wa fuskantar rikici tsakanin junansu, amma kuma abin ya }i samuwa. Taron sasantawa na }arshe wanda Mai Martaba Sarkin Zazzau ya jagoranta shi ne abu na }arshe, kafin ~ullar sabuwar wutar kiyayya tsakanin magoya bayansu a kwanaki.
Rahotanni sun nuna cewa, tsohon Gwamna Yarima ya ratsa garin Gusau ne tare da magoya bayansa a cikin jerin gwanon motoci, ana zargin suna la’antar manufofin gwamnatin Shinkafi tare da kiran sa da sunaye na ~atanci barkatai.
Duk da yake jami’an tsaro sun tsaurara matakan tsaro domin kauce tashin hankali a wannan rana da kuma yin fito-na-fito da juna. Yana da kyau al’ummar Jihar Zamfara da shugabaninsu su koyi darasi daga irin wutar rikicin siyasa wadda ta faru tsakanin magoya bayan Bafarawa da Wamakko a Sakkwato.
Wannan rikicin Sakkwato ya yi sanadiyyar asarar rayukan mutane har ishirin baya ga wasu da har yanzu suke kwance a asibiti, kuma an yi asarar dukiya ta miliyoyin Nairori.
Irin wannan fitina wadda magoya bayan Yarima da Shinkafi ke }o}arin rurutawa ba su ne za ta yi wa illa ba, illa ‘ya’yan talakawa da kuma sauran jama’ar da ba su san hawa ba su san sauka ba.
Masu nazarin siyasar Zamfara na ganin cewa, wannan da sauran ababen rashin jituwa na tsame hannun wasu daga cikin yaran tsohon Gwamna Yarima kacokan daga aiwatar da wani abu cikin gwamnatin Mahmuda Shinkafi ne dalilan wannan rashin jituwa, wanda kuma hakan bai yi musu da]i ba ko ka]an.
Tun farko dai tsohon Gwamna Yarima ya yi kuskure wajen shigowa Gusau, ya gudanar da taron gangamin siyasa ba tare da neman iznin jami’an tsaro da kuma ita kanta Gwamnatin jiha ba. Yana iya shigowa ya gudanar da taronsa a gidansa, ba tare da hayaniya ba domin kuwa ya saba da hakan, inji bayanin jami’an tsaro.
Wannan abin da ya faru ana iya kauce masa idan ba an yi da wata manufa ta takala ko janyo tashin hankali ba, domin kuwa a matsayinsa na shugaba yana da ha}}i mai yawa a kansa, wa]anda suka }unshi kiyaye doka da oda da samar da zaman lafiya a cikin al’umma da kuma bai wa shugabanni darajarsu da mutunta su.
Yanzu haka dai ~angaren Gwamna Shinkafi wanda shi ne ke da iko a kan shugabancin jam’iyyar ANPP da ke jagoranci jihar na tunanin korar wasu magoya bayan Yarima daga cikin jam’iyyar sakamakon zargin zagon }asa da suke yi wa gwamnatin da jam’iyya,wato suna ungulu ne da kan zabo na siyasarsu.
Hakan ta bayyana a ‘yan makonnin da suka gabata lokacin da kusan mafi rinjayen magoya bayan Ahmed Sani Yarima suka }aurace wa }addamar da babban kwamitin yi wa Gwamna Shinkafi yekuwar sake tsayawa a karo na biyu ko kuma “TWO TERMS’ da aka yi a otal ]in ‘City King’ da ke garin Gusau.
|angaren tsohon gwamna Ahmed Sani Yarima na dai yi wa na Gwamna Shinkafi kallon matsayin wa]anda suka ci amana kuma marasa al}awari, sakamakon yadda suka sa~a al}awarin da aka yi na rabon mu}amai ba tare da nuna bambanci ba, inji wata majiyar gidan Yarima.
To, amma kuma majiyar na ganin ba abin da ya dace illa a yi }o}arin janyo matsala da kuma haddasa rud]u tsakanin juna ta yadda har Gwamna Shinkafi ya cika shekaru hu]u ba zai iya gane komai ba.Wannan zargin da kuma cewa, Gwamna Shinkafi ya }i ya biya adashin da ya shiga da Yarima ne dalilan da suka sanya magoya bayan Yarima ke nuna ]an yatsa a maimakon guda biyu wato “ONE TERM” ke nan.
Haka kuma wasu daga cikin magoya bayan Yarima ~angare ]aya suna ganin cewa, ba wa]anda ke janyo rashin jituwar Gwamna Shinkafi da Sanata Yarima kamar wa]ansu manyan ‘yan siyasa wa]anda ke gindin gwamnati da wasu kwamishinoni da Yarima ya saukar tun farko amma yanzu Gwamna Shinkafi ya mayar da su cikin gwamnati da kuma wasu ‘yan majalisa da ke fushi da Yarima tun farko.
Ban da wannan ma, inji majiyar gwamnatin Shinkafi, akwai wasu da ake ganin suna da ala}a mai yawa ta jini da Yarima wa]anda kuma ake damawa da su a cikin wannan gwamnati. Wasu daga cikin su kuwa su ne mataimakin Gwamna Muhtari Anka da Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Zamfara, Alhaji Bature Gusau.
A bayanan rashin tabbas na wata majiya daga ~angaren Sanata Yarima, cewa, wa]anda suka fi tsana tare da Gwamnatin Mahmuda Shinkafi sun }unshi shugaban jam’iyyar ANPP ta jihar Zamfara Alhaji Ibrahim Mallaha, shugaban ma’aikatan fadar gwamnati, Musa Zubairu, Aliyu E.S. Kwamishina [an Jari, Ibrahim Na Bature Nahuche, Kwamishina Moriki, Sakataren Gwamnati Muhammad Bawa da wasu ‘yan majalisar dokokin jihar da kuma wasu manyan jami’an gwamnati da dattawan jam’iyyar ANPP wa]anda suka zama tamkar ana zargin suna tarna}i na samun daidaitawa tsakanin Yarima da Shinkafi.
Haka ma su kansu ~angaren Gwamna Shinkafi na zargin wasu daga cikin magoya bayan Sanata Ahmed Yarima da zama kanwa uwar gami na hana nasarar wata sassantawa ko barin Yariman gane gaskiyar lamari, musamman ma sun zama tamkar tushen ruruta wutar rikicin a tsakanin Yarima da Shinkafi.
Wa]anda sunayen nasu suka yi fice sun }unshi Alhaji Abdul’aziz Yari, Shehu J, Sani Garba Protocol, Lawal Jangebe, Munta}a Rini da kuma wasu da ke cikin gwamnatin Shinkafi amma suna fuska biyu wajen kai rahotannin sirri da ababen da ke faruwa a cikin gwamnati zuwa ga Yarima.
Lokaci ne yanzu da Sanata Ahmed Sani zai gane gaskiyar abin da ke faruwa tsakaninsa da Gwamna Shinkafi, domin kuwa tamkar yanzu idonsa a rufe yake na ababen da ake aikatawa. Yana da kyau ya lura da wa]anan ababen na }asa da illolinsu a nan gaba ga samuwar zaman lafiya ga Zamfarawa.
Shin haka ne aka yi masa a lokacin da yake nasa mulkin, ko yana ganin gwamnatin Shinkafi ta wasar yara ce, wadda ba za ta iya aikata komi ba. Ko kuma yana tunanin Shinkafi na da rauni ne ga aikata hukunci a kan wa]anda ya dace a hukunta?
Akwai mamaki da har Sanata Yarima zai fito fili ya }alubalanci gwamnan jiha a kafofin ya]a labarai cewa, idan har ya isa ya zo ya kama shi, maimakon magoya bayansa. Shin Yarima ya fi }arfin doka ne ko kuwa yana da wata ~oyyayar manufa ta nuna cewa, ba abin da za a yi masa?
Kada Yarima ya manta da cewa, lokacin da yake bisa karagar mulki, akwai wasu da dama, da suka dama shi suka shanye a iko da kuma gwamnati, amma sun girmama wannan ofishin nasa, ba wai domin tsoro ko rashin iya bangar siyasa ba ne, sun yi hakan ne domin neman zaman lafiya da kuma fahimtar juna a cikin al’ummar Zamfara.
Idan har lokacin mutane irin su, Janar Aliyu Gusau da Yahaya Gusau da Jabbi Maradun, Malam Yahaya Abdulkarim da Umaru Shinkafi da sauran wasu dattawan Jihar Zamfara na girmama shi a kan wannan kujerar, wane irin dalili yake da shi na }o}arin wula}anta Gwamna Mahmuda Shinkafi a yanzu?
Shin ko Yarima yana son mayar da abin da ya faru ne a Sakkwato domin samun iyar da wata manufa ko }o}arin ‘tauna aya, domin bai wa tsakuwa tsoro ne’. Sauran abin da ya rage ne na tsakanin jihohin guda biyu.
Ko ya manta da zargin irin adashin gata da suka shiga da shi da Adamu Aleiro da Wamakko domin neman tozarta tsohon Gwamna Bafarawa a lokacin mulkinsa na Jihar Sakkwato. Kodayake bai sami nasarar tozarta Gwamna Bafarawa ba duk kuwa da irin miliyoyin nairori na baitulmalin al’ummar Zamfara wa]anda ya ~atar a ]ora Wamakko bisa mulki, hakan yake son yi wa magajinsa, Gwamna Shinkafi a Zamfara?
Yadda yanzu aka mayar da Sakkwato a matsayin sansanin }ulle-}ulle a kan duk wani shiri na janyo ru]u da rikicin siyasa ga Zamfara, abin kunya da takaici ne. Wane irin alfanu ne zargin gwamnatin Wamakko ta bai wa yaran Yarima mafakar siyasa da ku]a]e domin su dawo gida su yi adawa da Gwamna Shinkafi?
Kuma wace irin hujja ce ga ‘ya’yan PDP na Jihar Sakkwato da aka samu cikin ayarin jerin gwanon motocin Yarima a Jihar Zamfara. Shin ko akwai wata manufa ce daban wadda ake yun}urin aiwatarwa a yanzu?
Dangane da wutar rikicin da ke ruruwa kuwa ba wani dalili da Yarima ko Mahmuda Shinkafi za su iya bai wa al’ummar Jihar Zamfara kan barin salwantar rayuka da dukiyar ‘ya’yansu saboda kwa]ayin tabbata a kan mulki.
Ya dace Yarima ya fahimci ya }are mulkinsa na shekaru takwas da da]ewa, a yanzu Shinkafi ne ke bisa, ba dalilin da zai janyo masa matsala ko kuma cewar ala dole sai ya koya masa ko kuma ya yi masa katsalanda.
A ~angaren Gwamna Mahmuda Shinkafi kuwa, ya cika sanyin hali na barin abin da ya zama wajibi gare shi ya wuce. Yaya zai zauna yana kallo ana }o}arin firgita al’ummar da ya rantse da Allah zai kula da mutuncinsu, zaman lafiyarsu da kuma kariyarsu da jin da]insu.
Ashe ba shi ne ya fa]a cewa, “Tamkar Jirgin }asa nake, duk abin da ya gitta man ba zan taka birki ba, zan wuce da shi.” Wannan kalamin kuwa ya manta da shi ne?
Matsayin Gwamna fa ba abin jin kunya ko tsoro ba ne kuma a matsayinsa na babban jami’in tsaro ga al’ummarsa, dole ne ya taka wa Yarima da magoya bayansa birki a }o}arinsu na zargin janyo fitina da tashin hankali a cikin al’umma. Tsarin mulki ya ba shi duk dama wadda ta dace, irin wadda shi kansa Yarima ya yi amfani da ita ga firgita Salihu Maibuhu Gummi da wasu sauran ‘yan adawarsa.
Ya dace Gwamna Shinkafi ya ji tsoron Allah domin hana manyan jami’ansa takalar magoya bayan Yarima idan har hakan na faruwa. Wato su daina amfani da }arfin gwamnatin wajen musguna musu. Yana da kyau a yi adalci, a kuma tuna da matsayin gaba na shugabancin da babu zalunci ba son rai.
Mulki kowane iri yana iya ]orewa amma fa ban da na zalunci. Yana da kyau a hana a cutar da wa]anda suka fito suka za~i al}iblarsu. Rashin samun goyon bayan yaran Yarima ba shi ne }arshen siyasarsa ko fa]uwar darajar gwamnatinsa ba.
Wa]anan da sauran ababen da suka faru ne dalilan rashin jituwar da ake ta faman ganin an kasa kai }arshenta. Ba shakka wannan idan har ya ci gaba zai yi wa jihar da kuma al’ummar jihar lahani ga samun zaman lafiya da kuma ci gabanta.
Muhimmin abin da ya dace shi ne ci gaba da aiwatar da ayyukan raya }asa da kuma samar da ci gaban }asa. Ya ]auki darasi daga Bafarawa wajen aiwatar da ayyukan ci gaban }asa ga al’umma, ba wai cika aljifansu ba. Idan har yana ganin wata barazana ne ya koma ga Allah wajen tallafa masa.
Darasi mai yawa zai koya bayan kammala ayyukan raya }asa da kuma ci gaban al’ummarsa, wasu daga ciki su ne irin wa]anda yanzu Bafarawa ke gani ga Sakkwatawa na sakkayar ayyukan alheri da ya aikata garesu, kuma ba shakka zai sami kyakkyawan sakamako nan gaba.
Yusuf Dingya]i, ]an jarida ne mai zaman kansa da ke zaune a lamba 88 titin Emir Yahaya, Sakkwato.
 


 

 

 

©2005 New Nigerian Newspapers Limited.

Webmasters: Emmanuel C. Bello & Suleiman A. Adamu