|
|
|
Rikicin
Siyasar Zamfara: Ko Yarima Da Shinkafi Za Su Koyi Darasi?
A
yanzu kam ta fito fili na wutar }iyyaya da rikici wadda ke ci gaba da ruruwa a
tsakanin tsohon Gwamnan Zamfara, Alhaji Ahmed Sani Yariman Bakura da kuma Gwamna
Mahmuda Aliyu Shinkafi. Wannan rikicin siyasa ya ]auko sabon salon kan yadda ake
amfani da bangar siyasa domin neman huce fushi da cimma manufa ta yi wa zaman
lafiyar Jihar Zamfara barazana.
Rashin ga-maciji da ke tsakanin shugabannin biyu ya fara kai ma}ura ne sakamakon
irin yadda magoya bayansu ke jifar juna da manganganun ~atanci na Allah wadai da
kuma suka a kan manufofin shugabannin, abin da ake kamantawa da cewa, ya fara
zafi.
Rashin jituwa tsakanin Sanata Yarima da tsohon mataimakinsa, Gwamna Shinkafi, ya
samo asali ne jim ka]an bayan shigowar sabuwar gwamnati ne, inda ake zargin }o}arin
katsalanda wajen gudanarwa da tsohon Gwamna Yarima yake yi wa gwamnatin Shinkafi.
Kodayake lamarin ya fara ne kamar wasa, sai ga shi ‘}aramar magana ta koma babba’,
tun tafiya ba ta yi nisa ba, an fara raba hannun riga tsakanin juna. Duk da yake
a lokaci mai tsawo, shugabannin sun fito sun }aryata wata rashin jituwa
tsakaninsu.
Tsohon Gwamna Ahmed Sani ne ya fara }aryata jita-jitar a lokacin da ya ziyarci
ofishin jaridar Trust da ke Abuja. Ya fito fili ya tabbatar wa duniya cewa,
Gwamna Shinkafi }anensa wanda ya rena kuma har yanzu yake goya masa baya ga duk
manufofinsa. Domin haka, inji Yarima, “ba wani sa~ani tsakaninmu, illa dai
surutan mutane ne da ke son janyo matsala ga juna”.
Shi kansa Gwamna Mahmuda Shinkafi ya fa]i irin wannan a hirarsa da jaridar
Gaskiya Ta Fi Kwabo a Kaduna, cewa da shi da Yarima uwa ]aya uba ]aya ne, kuma
ainihi Yarima na goyon bayan gwamnatinsa, domin haka ba wani sa~ani ko rashin
fahimta tsakaninsu.
Haka ma baki da baki Gwamna Shinkafi ya shaida mini a wata hirar da muka yi a
cikarsa shekara ]aya bisa karagar mulkin Jihar Zamfara cewa, yana mamaki na masu
kawo surutan ba su ga maciji da shi da tsohon mai gidansa, Yarima, domin tun
farko shi ba mutum ne mai surutu ko ]aukar tsegumi ba. A ra’ayinsa wannan
jita-jitar ana ya]a ta ne domin cimma wata manufa ta samun abinci da haddasa
ru]u da fitina tsakanin shugabanni.
Gwamna Shinkafi ya ce, “ba wani dalilin da zai sanya in cuci Yarima domin tun
farko na bi Yarima kuma na yi masa ]a’a. Allah Ya hana cuta, Ya kuma hana ka
bari a cuci wani. To, yaya zan fa]i wani mugun kalami a kan Yarima”.
Gwamna Shinkafi ya rufe da cewa, “idan har ka tambayi Yarima, abin da na yi masa,
ba zai ce ga shi ba, haka ni ma idan ka tambaye ni, mene ne tsakanina da shi, ba
zan fa]a ba”.
To, sai dai abin mamaki wannan duk ta canza domin kuwa kowanensu ya fito fili
yanzu ya nuna cewa, ba shiri a tsakaninsu, kuma duk wani abin da ake ~oyewa na
rashin fahimtar ya bayyana.
Tsohon Gwamna Ahmed Sani Yariman Bakura dai yana zargin Gwamna Shinkafi da
mu}arrabansa da kauce wa al}awarin da suka yi na samar da fahimtar juna da ha]in
gwiwa wajen aiwatar da gwamnati a tsakaninsu.
Haka ma ya yi zargin cewa, ana }untata wa magoya bayansa ta hanyar kora daga
aiki da kuma tsare wasu a gidan yari ba tare da wani dalili ba duk a sakamakon
adawarsu ga wasu manufofin Gwamnatin Mahmuda Shinkafi.
Haka ma Yariman Bakura na ganin ba a yi masa adalci ba na yadda aka raba wasu
mu}amai na siyasa a }ananan hukumomin mulki da kuma shugabancinsu ba tare da
tuntu~ar sa ko ba shi dama ba.
Ahmed Sani Yarima Bakura ya shafe shekaru takwas yana mulkin Jihar Zamfara, kuma
a tsawon lokacin mulkinsa ya fuskanci rikita-rikitar siyasa iri-iri ta rashin
ingantacciyar manufa wajen aiwatar da tsarin ci gaban al’umma da kuma zargin
watsi da bin }a’ida a cikin mulki.
A tsawon mulkinsa, ana zargin ya fi mayar da hankali ne ga cika aljifan magoya
bayansa da sauran ‘yan maular siyasa, maimakon aiwatar da ayyukan raya }asa da
kuma ci gaba a Jihar Zamfara. Wannan kuwa ya janyo talauci mai yawa a cikin ‘yan
siyasa da al’umma.
Wa]anda suke da masaniya kan Yariman Bakura sun tabbatar da cewa, ba ba}on
rikicin siyasa ne ba, sai dai yana da saurin hannu wajen shawo kan matsala fiye
da duk wanda ke cikin gwamnatinsa. Haka ma Yariman Bakura na da kusanci da
kafofin ya]a labarai saboda yadda ya yi tashe kan batun }ir}iro shari’a lokacin
mulkinsa.
Yarima ya fuskanci adawa ta zahiri a ciki da wajen gwamnatinsa daga wasu da ke
ganin bai dace na yadda yake mulkin jihar ba, duk da yake daga cikinsu ne suka
yi sanadiyyar hawansa bisa karagar mulki. Daga cikinsu akwai marigayi Abubakar [akingari,
Ibrahim Nabature Nahuce, Sanata Sa’idu Dansadau, Aliyu E.S Mafara, Isan Mayana
Gusau, Ibrahim Ruwan Dorawa, Mu’azu Mayana, Salihu Maibuhu Gummi, Sanata Lawal
Shu’aib da sauran wasu da suka riga mu gidan gaskiya ko kuma ke da rai har yanzu.
Abin tambaya a nan shi ne shin Yarima ya zama gangar rikici ne wadda ba ta iya
zama sai an buga. Babbar matsala ]aya ita ce gano ainihin tushen haddasa
matsalar da kuma abin da ya janyo wannan gaba da juna.
Wasu masu nazarin siyasar Zamfara na ta’alla}a wannan kan faruwar ababe da yawa,
masu muhimmanci, su ne zargin katsalanda da kuma yawan gori da tsohon gwamna
Yarima ke yi wa Shinkafi a cikin gwamnatinsa. Wasu kuma na ganin irin ayyukan ci
gaba da raya }asa wa]anda ya dace tun farko Yarima ya aiwatar, amma yanzu kuma
Gwamna Shinkafi yake gudanarwa. Wannan na ba}anta rayukan magoya bayan Yarima.
Na }arshe wanda shi ne, tamkar gaskiyar lamari, shi ne tseguma da kuma munafucin
siyasa da ya]a jita-jitar da ake yi, ne tushen wannan matsala ganin yadda wasu
daga cikin magoya bayan shugabannin biyu ke ya]a jita-jita ko kuma ke }ir}iro da
}arerayi a kan juna.
Wannan matsala da dalilan ne suka haddasa dakatar da wasu manyan jami’an
gwamnati a baya, ya sanya ~angaren Yarima ganin cewa, Gwamna Mahmuda Shinkafi ya
sa~a al}awarin raba daidai na aiwatarwa ta gwamnati, da kuma janyo ruruta wutar
fitina da haddasa mummunan rikici a kan juna.
Wasu daga cikin dalilan kuwa sun }unshi binciken gano yadda aka kashe ma}udan
ku]a]e ba tare da wani abin a-zo-a-gani ba a kan wasu kwangiloli a lokacin
gwamnatin Yarima wanda Majalisar Dokokin Jihar Zamfara ke yi, sai kuma sake
bayar da wasu kwangiloli da sake fasalta su da gwamnatin Mahmuda Shinkafi ta yi.
Akwai canjin wuraren aiki masu tsoka zuwa wasu wurare da ake yi wa la}abi na
ya-ku-bayi, ko kuma kulawa ta ‘ya’yan Mowa da na Bora da ake zargin ana yi wa
wasu jami’an gwamnati da ke da biyayya ga Yarima, duk sun }ara taimakawa kan
ya]a labarai na cewa, Gwamna Shinkafi na }o}arin tozarta Yarima da magoya
bayansa. A dalilan wannan, an }ara zurfafa wannan fitina.
Farkon wannan rikici tsakanin Yarima da Shinkafi, wasu muhimman mutane a cikin }asa
sun yi }o}arin sassantawa domin kauce wa fuskantar rikici tsakanin junansu, amma
kuma abin ya }i samuwa. Taron sasantawa na }arshe wanda Mai Martaba Sarkin
Zazzau ya jagoranta shi ne abu na }arshe, kafin ~ullar sabuwar wutar kiyayya
tsakanin magoya bayansu a kwanaki.
Rahotanni sun nuna cewa, tsohon Gwamna Yarima ya ratsa garin Gusau ne tare da
magoya bayansa a cikin jerin gwanon motoci, ana zargin suna la’antar manufofin
gwamnatin Shinkafi tare da kiran sa da sunaye na ~atanci barkatai.
Duk da yake jami’an tsaro sun tsaurara matakan tsaro domin kauce tashin hankali
a wannan rana da kuma yin fito-na-fito da juna. Yana da kyau al’ummar Jihar
Zamfara da shugabaninsu su koyi darasi daga irin wutar rikicin siyasa wadda ta
faru tsakanin magoya bayan Bafarawa da Wamakko a Sakkwato.
Wannan rikicin Sakkwato ya yi sanadiyyar asarar rayukan mutane har ishirin baya
ga wasu da har yanzu suke kwance a asibiti, kuma an yi asarar dukiya ta
miliyoyin Nairori.
Irin wannan fitina wadda magoya bayan Yarima da Shinkafi ke }o}arin rurutawa ba
su ne za ta yi wa illa ba, illa ‘ya’yan talakawa da kuma sauran jama’ar da ba su
san hawa ba su san sauka ba.
Masu nazarin siyasar Zamfara na ganin cewa, wannan da sauran ababen rashin
jituwa na tsame hannun wasu daga cikin yaran tsohon Gwamna Yarima kacokan daga
aiwatar da wani abu cikin gwamnatin Mahmuda Shinkafi ne dalilan wannan rashin
jituwa, wanda kuma hakan bai yi musu da]i ba ko ka]an.
Tun farko dai tsohon Gwamna Yarima ya yi kuskure wajen shigowa Gusau, ya gudanar
da taron gangamin siyasa ba tare da neman iznin jami’an tsaro da kuma ita kanta
Gwamnatin jiha ba. Yana iya shigowa ya gudanar da taronsa a gidansa, ba tare da
hayaniya ba domin kuwa ya saba da hakan, inji bayanin jami’an tsaro.
Wannan abin da ya faru ana iya kauce masa idan ba an yi da wata manufa ta takala
ko janyo tashin hankali ba, domin kuwa a matsayinsa na shugaba yana da ha}}i mai
yawa a kansa, wa]anda suka }unshi kiyaye doka da oda da samar da zaman lafiya a
cikin al’umma da kuma bai wa shugabanni darajarsu da mutunta su.
Yanzu haka dai ~angaren Gwamna Shinkafi wanda shi ne ke da iko a kan shugabancin
jam’iyyar ANPP da ke jagoranci jihar na tunanin korar wasu magoya bayan Yarima
daga cikin jam’iyyar sakamakon zargin zagon }asa da suke yi wa gwamnatin da
jam’iyya,wato suna ungulu ne da kan zabo na siyasarsu.
Hakan ta bayyana a ‘yan makonnin da suka gabata lokacin da kusan mafi rinjayen
magoya bayan Ahmed Sani Yarima suka }aurace wa }addamar da babban kwamitin yi wa
Gwamna Shinkafi yekuwar sake tsayawa a karo na biyu ko kuma “TWO TERMS’ da aka
yi a otal ]in ‘City King’ da ke garin Gusau.
|angaren tsohon gwamna Ahmed Sani Yarima na dai yi wa na Gwamna Shinkafi kallon
matsayin wa]anda suka ci amana kuma marasa al}awari, sakamakon yadda suka sa~a
al}awarin da aka yi na rabon mu}amai ba tare da nuna bambanci ba, inji wata
majiyar gidan Yarima.
To, amma kuma majiyar na ganin ba abin da ya dace illa a yi }o}arin janyo
matsala da kuma haddasa rud]u tsakanin juna ta yadda har Gwamna Shinkafi ya cika
shekaru hu]u ba zai iya gane komai ba.Wannan zargin da kuma cewa, Gwamna
Shinkafi ya }i ya biya adashin da ya shiga da Yarima ne dalilan da suka sanya
magoya bayan Yarima ke nuna ]an yatsa a maimakon guda biyu wato “ONE TERM” ke
nan.
Haka kuma wasu daga cikin magoya bayan Yarima ~angare ]aya suna ganin cewa, ba
wa]anda ke janyo rashin jituwar Gwamna Shinkafi da Sanata Yarima kamar wa]ansu
manyan ‘yan siyasa wa]anda ke gindin gwamnati da wasu kwamishinoni da Yarima ya
saukar tun farko amma yanzu Gwamna Shinkafi ya mayar da su cikin gwamnati da
kuma wasu ‘yan majalisa da ke fushi da Yarima tun farko.
Ban da wannan ma, inji majiyar gwamnatin Shinkafi, akwai wasu da ake ganin suna
da ala}a mai yawa ta jini da Yarima wa]anda kuma ake damawa da su a cikin wannan
gwamnati. Wasu daga cikin su kuwa su ne mataimakin Gwamna Muhtari Anka da
Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Zamfara, Alhaji Bature Gusau.
A bayanan rashin tabbas na wata majiya daga ~angaren Sanata Yarima, cewa,
wa]anda suka fi tsana tare da Gwamnatin Mahmuda Shinkafi sun }unshi shugaban
jam’iyyar ANPP ta jihar Zamfara Alhaji Ibrahim Mallaha, shugaban ma’aikatan
fadar gwamnati, Musa Zubairu, Aliyu E.S. Kwamishina [an Jari, Ibrahim Na Bature
Nahuche, Kwamishina Moriki, Sakataren Gwamnati Muhammad Bawa da wasu ‘yan
majalisar dokokin jihar da kuma wasu manyan jami’an gwamnati da dattawan
jam’iyyar ANPP wa]anda suka zama tamkar ana zargin suna tarna}i na samun
daidaitawa tsakanin Yarima da Shinkafi.
Haka ma su kansu ~angaren Gwamna Shinkafi na zargin wasu daga cikin magoya bayan
Sanata Ahmed Yarima da zama kanwa uwar gami na hana nasarar wata sassantawa ko
barin Yariman gane gaskiyar lamari, musamman ma sun zama tamkar tushen ruruta
wutar rikicin a tsakanin Yarima da Shinkafi.
Wa]anda sunayen nasu suka yi fice sun }unshi Alhaji Abdul’aziz Yari, Shehu J,
Sani Garba Protocol, Lawal Jangebe, Munta}a Rini da kuma wasu da ke cikin
gwamnatin Shinkafi amma suna fuska biyu wajen kai rahotannin sirri da ababen da
ke faruwa a cikin gwamnati zuwa ga Yarima.
Lokaci ne yanzu da Sanata Ahmed Sani zai gane gaskiyar abin da ke faruwa
tsakaninsa da Gwamna Shinkafi, domin kuwa tamkar yanzu idonsa a rufe yake na
ababen da ake aikatawa. Yana da kyau ya lura da wa]anan ababen na }asa da
illolinsu a nan gaba ga samuwar zaman lafiya ga Zamfarawa.
Shin haka ne aka yi masa a lokacin da yake nasa mulkin, ko yana ganin gwamnatin
Shinkafi ta wasar yara ce, wadda ba za ta iya aikata komi ba. Ko kuma yana
tunanin Shinkafi na da rauni ne ga aikata hukunci a kan wa]anda ya dace a
hukunta?
Akwai mamaki da har Sanata Yarima zai fito fili ya }alubalanci gwamnan jiha a
kafofin ya]a labarai cewa, idan har ya isa ya zo ya kama shi, maimakon magoya
bayansa. Shin Yarima ya fi }arfin doka ne ko kuwa yana da wata ~oyyayar manufa
ta nuna cewa, ba abin da za a yi masa?
Kada Yarima ya manta da cewa, lokacin da yake bisa karagar mulki, akwai wasu da
dama, da suka dama shi suka shanye a iko da kuma gwamnati, amma sun girmama
wannan ofishin nasa, ba wai domin tsoro ko rashin iya bangar siyasa ba ne, sun
yi hakan ne domin neman zaman lafiya da kuma fahimtar juna a cikin al’ummar
Zamfara.
Idan har lokacin mutane irin su, Janar Aliyu Gusau da Yahaya Gusau da Jabbi
Maradun, Malam Yahaya Abdulkarim da Umaru Shinkafi da sauran wasu dattawan Jihar
Zamfara na girmama shi a kan wannan kujerar, wane irin dalili yake da shi na }o}arin
wula}anta Gwamna Mahmuda Shinkafi a yanzu?
Shin ko Yarima yana son mayar da abin da ya faru ne a Sakkwato domin samun iyar
da wata manufa ko }o}arin ‘tauna aya, domin bai wa tsakuwa tsoro ne’. Sauran
abin da ya rage ne na tsakanin jihohin guda biyu.
Ko ya manta da zargin irin adashin gata da suka shiga da shi da Adamu Aleiro da
Wamakko domin neman tozarta tsohon Gwamna Bafarawa a lokacin mulkinsa na Jihar
Sakkwato. Kodayake bai sami nasarar tozarta Gwamna Bafarawa ba duk kuwa da irin
miliyoyin nairori na baitulmalin al’ummar Zamfara wa]anda ya ~atar a ]ora
Wamakko bisa mulki, hakan yake son yi wa magajinsa, Gwamna Shinkafi a Zamfara?
Yadda yanzu aka mayar da Sakkwato a matsayin sansanin }ulle-}ulle a kan duk wani
shiri na janyo ru]u da rikicin siyasa ga Zamfara, abin kunya da takaici ne. Wane
irin alfanu ne zargin gwamnatin Wamakko ta bai wa yaran Yarima mafakar siyasa da
ku]a]e domin su dawo gida su yi adawa da Gwamna Shinkafi?
Kuma wace irin hujja ce ga ‘ya’yan PDP na Jihar Sakkwato da aka samu cikin
ayarin jerin gwanon motocin Yarima a Jihar Zamfara. Shin ko akwai wata manufa ce
daban wadda ake yun}urin aiwatarwa a yanzu?
Dangane da wutar rikicin da ke ruruwa kuwa ba wani dalili da Yarima ko Mahmuda
Shinkafi za su iya bai wa al’ummar Jihar Zamfara kan barin salwantar rayuka da
dukiyar ‘ya’yansu saboda kwa]ayin tabbata a kan mulki.
Ya dace Yarima ya fahimci ya }are mulkinsa na shekaru takwas da da]ewa, a yanzu
Shinkafi ne ke bisa, ba dalilin da zai janyo masa matsala ko kuma cewar ala dole
sai ya koya masa ko kuma ya yi masa katsalanda.
A ~angaren Gwamna Mahmuda Shinkafi kuwa, ya cika sanyin hali na barin abin da ya
zama wajibi gare shi ya wuce. Yaya zai zauna yana kallo ana }o}arin firgita
al’ummar da ya rantse da Allah zai kula da mutuncinsu, zaman lafiyarsu da kuma
kariyarsu da jin da]insu.
Ashe ba shi ne ya fa]a cewa, “Tamkar Jirgin }asa nake, duk abin da ya gitta man
ba zan taka birki ba, zan wuce da shi.” Wannan kalamin kuwa ya manta da shi ne?
Matsayin Gwamna fa ba abin jin kunya ko tsoro ba ne kuma a matsayinsa na babban
jami’in tsaro ga al’ummarsa, dole ne ya taka wa Yarima da magoya bayansa birki a
}o}arinsu na zargin janyo fitina da tashin hankali a cikin al’umma. Tsarin mulki
ya ba shi duk dama wadda ta dace, irin wadda shi kansa Yarima ya yi amfani da
ita ga firgita Salihu Maibuhu Gummi da wasu sauran ‘yan adawarsa.
Ya dace Gwamna Shinkafi ya ji tsoron Allah domin hana manyan jami’ansa takalar
magoya bayan Yarima idan har hakan na faruwa. Wato su daina amfani da }arfin
gwamnatin wajen musguna musu. Yana da kyau a yi adalci, a kuma tuna da matsayin
gaba na shugabancin da babu zalunci ba son rai.
Mulki kowane iri yana iya ]orewa amma fa ban da na zalunci. Yana da kyau a hana
a cutar da wa]anda suka fito suka za~i al}iblarsu. Rashin samun goyon bayan
yaran Yarima ba shi ne }arshen siyasarsa ko fa]uwar darajar gwamnatinsa ba.
Wa]anan da sauran ababen da suka faru ne dalilan rashin jituwar da ake ta faman
ganin an kasa kai }arshenta. Ba shakka wannan idan har ya ci gaba zai yi wa
jihar da kuma al’ummar jihar lahani ga samun zaman lafiya da kuma ci gabanta.
Muhimmin abin da ya dace shi ne ci gaba da aiwatar da ayyukan raya }asa da kuma
samar da ci gaban }asa. Ya ]auki darasi daga Bafarawa wajen aiwatar da ayyukan
ci gaban }asa ga al’umma, ba wai cika aljifansu ba. Idan har yana ganin wata
barazana ne ya koma ga Allah wajen tallafa masa.
Darasi mai yawa zai koya bayan kammala ayyukan raya }asa da kuma ci gaban
al’ummarsa, wasu daga ciki su ne irin wa]anda yanzu Bafarawa ke gani ga
Sakkwatawa na sakkayar ayyukan alheri da ya aikata garesu, kuma ba shakka zai
sami kyakkyawan sakamako nan gaba.
Yusuf Dingya]i, ]an jarida ne mai zaman kansa da ke zaune a lamba 88 titin Emir
Yahaya, Sakkwato.
|